Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Tashar talabijin ta Aljazeera dake kasar Qatar ta nakalto Janar Burhan yana fadar haka a sakonsa na taya mutanen kasar murnar sallar Idi karama.
Har’ila yau labarin ya kara da cewa shugaban ya bayyana cewa a shirye yake ya hada kai da dukkan jam’iyyun siyasa wadanda suke son ci gaban kasar Sudan da kuma ganin cewa ta fita daga cikin matsalplom da ta fama da su a halin yanzu.
A wani bangare kuma shugaban Burhan y ace dole ne a sauya wasu dokokin kasar saboda kawo karshen rikicin kabilanci wanda ya ki ci yaki cinyewa a wasu sassan kasar.
342/