Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Litinin

2 Mayu 2022

12:51:59
1254169

Rikici ya Barke A Birnin Faris Bayan Da Dubban Mutane Suka Fito Zanga-zangar Adawa Da Makron

Kungiyoyin kwadago da ta dalibai a kasar faransa sun jagoranci babbar zanga zangar nuna adawa da sabon zababben shugaban kasar Emanuel macron a birnin faris inda suka bukaci ya kara albashin ma’aikata . da kara tallafawa ayyukan da gwamnati ke yi wa jama’a da kuma kare manufofin da suka dace da yanayin zamantakewar jama’a.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Rikici ya barke ne tsakanin wasu matasa da suke sanya da bakaken kaya da jami’an yan sanda inda aka farfasa tagogin shaguna inda wuta take ta fitowa, inda suke dauke da kwaleye da aka zana kalaman nuna adawa da tsarin jari hujja, wannan yasa yan sanda suka yi amfani da barkunon tsohuwa wajen tarwatsa masu zanga-zangar

Su mana masu adawa da manufofin siyasar Makron sun yi zanga-zangar nuna adawa das hi a kan tituna a birane daban –daban na kasar faransa a lokacin yakin neman zabe da kuma ranar da aka gudanar da zabe a aksar, inda a zagaye na biyu ne Makron ya kayar da abokiyar hammayarsa Marine Le pen da hakan ya bashi damar ci gaba da kasancewa a kujarar shugabancin kasar.

342/