Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Da yake sanar da hakan ministan tsaron Rashar, Sergueï Choïgou, ya kuma bukaci dakarun Kiev, dasu ajiye makamai.
Kafin hakan dai ma’aikatar tsaron Rashar ta sanar yau Talata da kaddamar da gomman hare hare a wasu cibiyoyi da sansanonin soji a gabashin Ukraine a cikin daren jiya.
A nasa bangare Shugaban kasar Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya ce zasu ci gaba da jan daga domin kare kasarsu.
342/