Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

22 Maris 2022

18:17:38
1241639

WHO, Ta Caccaki Kasashen Turai Kan Dage Matakan Yaki Da Korona

Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta caccaki wasu kasashen turai kan dage matakan yaki da annobar korona cikin sauri kuma ‘’ba wani shiri’’.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - WHO, ta ce ba ta ji daidin wannan matakin ba da Kasashen turan da dama ne da suka hada da Jamus, Faransa, Italiya da kuma Biritaniya suka dauka ba tare da wani shiri ba, a daidai lokacin da kuma suka fara fuskantar karuwar masu kamuwa da cutar karamin nau’in BA.2

Yayin wani taron manema labarai a Moldavie, darektan hukumar ta WHO, rashen turai, Hans Kluge, ya su ne bibiyar halin da ake ciki a nahiyar.

A halin da ake ciki dai yawan masu kamuwa da cutar ta korona ya karu a kasashe 18 daga cikin 53 na yankin a cewar WHO.

342/