Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Talata

15 Maris 2022

19:54:54
1239616

Kasar Chadi Ta Mika Wa Kotun Duniya Ta Manyan Laifuka Kwamandan Kungiyar Anti-Balaka Ta Kasar Afirka Ta Tsakiya

A jiya Litinin ne dai kasar ta Chadi ta sanar da mika Maxime Mokom wanda shi ne shugaban kungiyar da ke dauke da makamai a kasar Afirka Ta Tsakiya, zuwa ga kotun duniya ta manyan laifuka ( ICC).

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Shi dai Mokom da sauran ‘yan kungiyarsa ana zarginsu da aikata laifuka akan bil’adama a birnin Bangul na kasar Afirka Ta Tsakiya a shekarun 2013 da kuma 2014,kamar yadda sanarwar kotun ta manyan laifuka mai matsuguni a birnin Hague ta bayyana.

Kasar Afirka Ta Tsakiya Ta Fada Cikin Rikici Da Fadace-fadace bayan kifar da shugaban kasar Francois Bozize a 2013, ta hannun kungiyar Seleka.

Tun bayan da kasar ta sami ‘yanci daga ‘yan mulkin mallakar Faransa a 1960’s, ta kasance mai fama da talauci duk da dimbin arzikin da Allah ya huwace mata.

342/