Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban tawagar tattaunawar kasar Ukrain Mykhailo Podolyak yana fadar haka a shafinsa na Twitter a safiyar yau Litinin.
Ya kuma kara da cewa wannan shi ne taron tattaunawan kan tsagaiuta budewa juna wuta na 4 kenan tun bayan fara yakin kwanaki kimani 18 da suka gabata.
Banda haka Mykhailo Podolyak ya ce banda haka an sami ci gaba a tattaunawar baya, kuma a cikin ‘yan kwanakin masu zuwa muna saran za’a sami ci gaban da bangarorin biyu zasu amince a kansu.
Har’ila yau a bangaren kasar Rasha kuma, kakakin gwamnatin kasar Dmitry Peskov ya bada sanarwan cewa za’a koma kan teburin tattaunawa a safiyar yau Litinin a kasar Belerus kamar yadda aka saba.
342/