Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Wannan yana zuwa ne bayan da a yan kwanakin nan yarima mai jiran gado na kasar Saudiya Mohammad Bin Salman ya shaidawa mujallar Atlantic Magazine cewa Saudiya ba ta kallon Isra’ila a matsayin abokiyar gaba. Wanda wannan matakin ya harzuka kungiyoyin gwagwarmaya na falasdinu
A hirar da yayi da gidan talabijin din Press TV Davood shahab ya bayyana daidaita hulda da Isra’ila a matsayin cin Amanar falasdinawa larabawa da alummar musulmi
Daga karshe ya nuna cewa ba mu amince da duk wata kulla hulda da gwamnatin mamaya ba , domin kasancewar Isara’ila a yankin falasdinu baya bisa doka.
342/