Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Litinin

31 Janairu 2022

19:25:09
1224654

M D D Ta Yabawa Iran Da Pakistan Kan Karamcin Da Su Ke Nunawa Alummar Afghanistan

Babban sakatare Janar din M D D Antonio Gutterres ya fadi cewa Kasashen Iran da Pakistan sun nuna karamcin dab a za’a taba mantawa das hi ba game da yadda suka karbi bakunci miliyoyin Alummar Afghanistan a kasashen su.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - Ya kara da cewa kasar Iran tana karba daururuwan Afghnawa yan gudu hijira duk da takunkumin tattalin arziki da take ciki, da kuma rashin samun hadin kai hukumomi na kasa da kasa da alhakin hakan ya rataya awuyansu, wanda a lokacin yanayi na sanyi ma takara rubanya ayyukan jinkai da take yi a kasar ta Afghanistan

Da yake bayani a wajen taron kwamitin tsaro na Majalisar dinkin duniya a fakon makon nan Guterres ya fadi cewa bazan taba mantawa da irin karamcin da kasashen iran iran suka nuna ba yadda suka kwashe shekaru suna maraba da miliyoyin yan gudun hijirar kasar Afghanistan a kasarsu.

Daga karshe ya nuna cewa akwai bukatar hada hannu tsakanin Majalisar da alummar duniya wajen ganin an fitar da kasar Afghanistan daga mawuyacin halin da take ciki.

342/