Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : Hausatv
Asabar

25 Disamba 2021

14:12:13
1212167

Kasashe 125 Sun Goyi Bayan Ci Gaba Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da Isra’ila Ta Tafka

Rahotanni sun bayyana cewa da dukkan rinjaye sama da kasashe 125 ne suka nuna goyon bayansu game da ci gaba da gudanar da bincike da hukumar Kare hakkin bil adama ta majalisar dinkin duniya ke yi kan zargin tafka laifukan yaki da HKI ta yi kan Alummar Falasdinu ciki har wuce gona da irin na kwanaki 11 da ta yi a yankin Gaza a farkon wannan shekarar.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {a.s} - ABNA - A watan mayu ne sojojin Isra’ila suka yi ruwan bama- bamai a yankin Gaza na tsawon kwanaki 11 cur, da ya kai ga kashe mutane 260, ciki hard a yara kanana 66, wanda bayan yakin ne mambobi 47 na hukumar kare hakkin bil adama suka amince da fara gudanar da bincike kan laifukan yaki da sojojin Isra’ila suka tafka kan falasdinawa dake zaune a yankunan marasa galihu.

Bayan kada kuri’ar amincewar da jakadan falasdinu na dindindin a majalisar dinkin duniya Riyad Mansur ya yaba da mataki da mambobin majalisar suka dauka na yin watsi da kudurin da Isra’ila game da binciken, kuma ya gode musu game da amincewa da suka yi da kasafin kudin kan batun falasdinu , ciki har da batun kara yawan kudaden da ake bawa hukumar kula da yan gudun hijira falasdinawa ta majalisar Dinkin duniya Unrwa.

342/