Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Laraba

24 Nuwamba 2021

19:37:18
1201848

FAO Ta Gargadi Duniya Game Da Barazanar Karamcin Abinci

Hukumar kula da abinci da aikin gona ta Majalisar Dinkin Duniya, (FAO), ta bukaci kasashen duniya su zage damtse saboda babbar barazanar dake akwai ta fuskantar fari.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : A sabon rahoton da ta fitar hukumar ta ce, annobar korona, canjin yanayi da rikice rikice sun yi tasiri sosai kan harkar samar da abinci musamman a nahiyar Afrika.

A yankin kudancin Afrika, sama da mutane miliyan 80 ne zasu iya rasa samun abinci mai kyau idan aka fuskanci wani sabon tashin hankali a cewar FAO.

Dole ne kasashen da matsalar ta shafa su gabatar da wani da ya shafi abincin da suke samarwa a gida da wanda suke shigo da shi.

342/