Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Lahadi

21 Nuwamba 2021

15:30:17
1200827

Amurka Ta yi Kira Ga Shugabannin Kasashen Afrika Da su Bunkasa Tsarin Dimokradiya

Da yake bayani a wata ziyara da ya kai wasu kasashen Afrika, Antony Blinken sakataren harkokin wajen Amurka ya bayyana cewa Najeriya ta cancanci babban matsayi a duk inda ake tattauna muhimman batutuwa a nahiyar Afirka, kuma kasarsa a shirye take ta hada kai da Najeriya ba kamar yadda ake amfani da ita ba a baya.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Har ilya yau da yake bayani a Helkwatar hukumar habaka tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWA) Blinken ya bukacin kasashen yammacin Afrika da su yi watsi da mulkin kama karya, kuma su tabbatar an ingantaccen tsarin Dimokiradiya a kasashensu.

Blinken da yake ziyararsa ta farko a yankin kudu da Hamadar sahra a matsayinsa na sakataren wajen kasar Amurka ya fadi cewa kungiyoyi irin su ECOWAS, AU, SADAC da IGAD ya kamata su taka muhimmiyar rawa da ta dace, kuma su kasance suna da karfin fada a ji a muhawarorin da ake yi a duniya.

342/