Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Jaridar The Times ta Isra'ila ta nakalto wani jami'i na kusa da Firaministan Isra'ila Naftali Bennett yana cewa "Gwamnatin shugaban Amurka Joe Biden ba za ta hana gina matsugunan Yahudawa a yammacin gabar kogin Jordan ba.
Haka nan kuma a cewar Gwamnatin Bennett tana sa ran gwamnatin Biden na da niyyar sake bude karamin ofishin jakadancinta a birnin Kudus.
A ranar 27 ga Oktoba, kwamitin tsare-tsare na Ma'aikatar Yakin Isra'ila ta amince da gina gidaje 3,144 da ba bisa ka'ida ba a Yammacin Gabar Kogin Jordan.
Wannan ne dai karon farko tun bayan shugabancin Joe Biden, Isra’ila ta kudiri aniyar gina matsugunna yahuadawa a cikin yankunan Falastinawa da ke gabar yamma da kogin Jordan.
Yanzu haka dai akwai matsugunan yahudawa 13 da Isra’ila ta gina ba bisa ka'ida ba a Gabashin Kudus, da kuma wasu 253 a Yammacin Kogin Jordan, inda Yahudawa sama da 660,000 suke.
A karkashin dokokin kasa da kasa, ana daukar dukkan matsugunan Yahudawa da aka gina a cikin yankunan Falasdinawa da cewa aiki ne na mamaya wanda ba ya bisa ka’ida.
342/