Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Lahadi

17 Oktoba 2021

15:03:48
1189433

Amurka Tana Tsare Da ‘Yan Najeriya 11 Saboda Zargin Almundahana Da Kudaden Jama’a

Ma’aikatar shari’a a kasar Amurka ta bata sanarwan cewa tana tsare da ‘yan Najeriya 11 wadanda ake tuhuma da almundahana da kudaden jama’a da kuma zamba cikin amince, wanda ya shafi mutane fiye da 50, wadanda aka yi damfara na kudade kimani Dalar Amurla biliyon 9, duk a kasar ta Amurka.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto ma’aikatar sharia ta NewYork tana cewa an kama mutane 9 daga cikin su a birnin Newjessy a ranar 13 ga watan octoban da muke ciki, sannan daya kuma a jihar Texas.

Labarin ya kara da cewa yan Najeriya wadanda aka gurfanar da su a gaban kuliya a halin yanzu dangane da wannan shari'ar sun hada da Adedayo John, 32; Oluwadamilola Akinpelu, 26; Kazeem Raheem, 29; Morakinyo Gbeyide, 39; Warris Adenuga da aka Blue, 26.

Sauran sun hada da , Lateef Goloba, 27; Samsondeen Goloba, 29; Olawale Olaniyan, 41; Olawoyin Peter Olarewaju, 34 da kuma Emmanuel Oronsaye-Ajayi, 30.

342/