Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Laraba

13 Oktoba 2021

12:45:27
1188375

Ana Zargin Shugaban Kasar Brazil Da Cin Zarafin Bil-Adama A Kotun Duniya Ta ICC

Wani mai rajin kare mahalli ya shigar da korafi a gaban babbar kotun hukumta manyan laifukan yaki ta ICC na zargi shugaban kasar Brazil Jair Bosonaro da cin zarafin bil adama, saboda rawar da ya taka wajen lalata dajin Amazon.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : A cikin takardar koken da ya shigar a gaban kotun duniya dake birinin Hek, mai rajin kare mahalli din dan kasar Austiriya ya bukaci da a gudanar da bincike kan shugaban kasar Barazil da gwamnatinsa game da alakar da suke da shi kai tsaye da mummunan tasirin canjin yanayi da aka samu a duniya.

Har ila yau ya zo acikin takardar cewa Bolsonaro shi ke da alhakin lalata gandun daji mai fadin Mita Murabba’I 4000, da kuma karancin ruwan sama da ake samu a duk shekara, inda ya ci gaba har zuwa kashi 88 cikin dari daga lokacin da ya hau kan mulkin a shekara ta 2019. Zuwa yau.

342/