Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : parstoday
Litinin

4 Oktoba 2021

13:21:21
1185785

Amurka : Yawan Wadanda Yan Sanda Ke Gallazawa Ya Zarce Yadda Ake Tsammani­_The Lancet

Wani rahoton bincike na baya bayan nan da mujallar kiwon lafiya ta kasa da kasa wato "The Lancet" ta fitar ya nuna cewa, adadin mutanen da suka mutu a sanadiyyar cin zarafi da jami’an ‘yan sandan kasar Amurka suka yi musu, ya wuce wanda hukumomin kasar suka fitar.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Masu binciken sun gano cewa tun a shekarun 1980, an samu adadin mutanen da suka mutu sama da 17,000 a sakamakon gallazawar da ‘yan sandan Amurka suka yi musu.

Kusan kashi 60% na Amurkawa ‘yan asalin Afrika da suka mutu sakamakon muzgunawar ‘yan sandan, ko dai ba a bayyana su ba ko kuma an yi kuskure wajen kididdige su.

Rahoton ya kara da cewa, bayanan bogi ko kuma rashin kididdige wadannan mace-macen da aka samu zai kara boye girman mummunar matsalar nuna wariyar da hukumomin tabbatar da tsaron Amurka ke aikatawa.

342/