Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Laraba

22 Satumba 2021

16:20:29
1182330

Amurka Na Son Iran Ta Koma Yarjejeniyar Nukiliya Ta Hanyar Diflomasiya

Shugaban Amurka Joe Biden, ya yi alkawarin samar da kudaden yaki da annobar korona, da sauyin yanayi, sannan kuma ya yi alkawarin dawo da kasarsa a cikin yarjejeniyar nukiliyar Iran, amma da sharadin Iran za tayi hakan.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Mista Biden, ya bayyana hakan ne yayin jawabin da ya gabatar a babban taron MDD, da aka fara a wannan Talata.

‘’Tare da sauren manyan kasashen duniya, (Faransa, Biritaniya, Rasha da kuma China) Amurka na aiki ta hanyar diflomatsiyya domin dawo da Iran a cikin yarjejeniyar nukiliyar ta 2015 cikin tsanaki’’, inji shugaba Biden.

Saidai ya ce Amurka tana nan kan barkarta na hana Iran mallakar makamin nukiliya.

Kafin hakan dai kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Saïd Khatibzadeh, wanda ke halartar taron a birnin New York, ya bayyana cewa za’a koma tattaunawar farfado da yarjejeniyar Iran a cikin makonni masu zuwa.

342/