Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Haka zalika wakilan din din din na kasashen a majalisar dinkin duniya sun nuna rashin jin dadinsu game da yadda kasar Amurka ke ci gaba da take yarjejniyoyin da aka cimma matsaya a kai a shekara ta 1947 inda ta bukaci a mika shari’a zuwa ga kotun sasantawa domin yi wa bakin tubkar hanci.
Musamman ganin cewa mai masaukin baki hakkinta ne ta sanar da lokacin ga dukkan wakilan kasashen duniya da za su halarci zaman babban zauren majalsar dinkin duniya ko kuma aiki a majalisar.
Daga karshe kasashen guda 6 sun bayyana cewa an kafa majalisar dinkin duniya ne bisa girmamawa da mutunta ko wacce mamba dake cikinta ba tare da wani bambanci ba,, domin bai kamata ta yarda da duk wani nuna banbanci ko wariya tsakanin mambobin majalisar ba.
342/