Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti

Madogara : hausatv
Asabar

18 Satumba 2021

12:22:05
1180985

​Amurka Ta Sake Kakabawa Kungiyar Hizbullah Takunkumi Bayan Isar Man Fetur Din Iran Kasar Labanon

A cikin wata sanarwar da ma’aikatar baitulmalin Amurka ta fitar ya nuna cewa ofishinta dake kula da kadarorin kasashen waje ya fitar da sunayen mutane da kamfanonin da suke taimakawa kungiyar Hizbulla da kuma rudunar Quds ta dakarun kare juyin musulunci ta Iran kudade.

Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti {A.S} - ABNA : Daga cikin wadanda abin ya shafa akwai Morteza Minaye Hashemi wanda shi ne ma’ajin Amurka ke zargin yana taimakawa kungiyar Hizbullah, sai kuma kamfanin kasar China Yan SU Xuan da kuma Son jing da take zargin su da taimakawa Hashemi wajen bude asusun bankin.

Sakatare harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya fadi cewa Amurka ba za ta yi kasa a guiwa ba wajen sanya ido kan ayyuakansu, kuma za ta ci gaba da daukar tsauraran matakai na dakile ayyukan da suke gudanarwa, takunkuman sun hada da kwace kadarorinsu da kuma hana yin duk wata musayar kudade da su

Ita dai kungiyar Hizbullah ta dauki wannan matakin ne domin rage radadi da Al’ummar kasar suke ciki, da yake gab da tsada kasar cik, wanda kuma ya samo asali sakamakon matsalar tattalin arziki da kuma karancin makamashi da kasar take fama da su.

342/