Kamfanin dillancin labarai na Ahlul-Baiti{A.S} - ABNA : Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban ya na fadar haka a jiya jumma’a, ya kuma kara da cewa dangin Amurkawa kimani 3000 wadanda suka rasa rayukansu a hare-haren su na son a bayyana sakamakon binciken da aka gudanar kan hare-haren don su gano wadanda suke da hannu a cikin hare-haren don kuma karbar diyya daga wadanda suke goyon bayan yan ta’addan da suka kai hare-haren na 11/09/2001.
Kafin haka dai an bayyana cewa mutane 19 ne ‘yan kungiyar Al-Qa’ida suka shirya kuma suka kai hare-haren, sannan da dama daga cikinsu ‘yan kasar Saudiya ne.
342/