-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Tattakin Wadanda Basu Samu Zuwa Arba'in Ba A Shiraz
An gudanar da taron tattakin wadanda suka rasa halartat Arba'in na Husaini da safiyar yau Talata tare da halartar masoya da masu ƙaunar Aba Abdillahil Husain (AS) har zuwa harami mai tsarki na Shah Cheragh (AS) a Shiraz.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Yanayin Haramai Biyu Na Karbala Mai Girma, Wurin Haduwar Masoya
Kamfanin dillancin labarai na Ahl al-Bayt (AS) - ABNA -:
-
Sudan: Kawancen "Sumud" Da Daidaitawa: Bita Kan Ziyarar Shugabannin Kawancen "Sumud" Zuwa Isra’ila
"Sumud" kalma ce ta Larabci da ke nufin "juriya" ko "tsayin daka". A siyasance, "Sumud" wani kawance ne na kungiyoyin farar hula da suka fito a Sudan bayan yakin da ya barke a watan Afrilu 2023. Sunan cikakken kawancen shi ne: "Kawancen Farar Hula na Dimokuradiyya na Dakarun Juyin Juya Hali". Kawancen ya fito a tsakiyar shekarar 2025, kuma ya gabatar da kansa a matsayin "mai tsaka-tsaki" tsakanin bangarorin yaki a Sudan (sojojin kasa da dakarun tallafi na gaggawa). Ana sukar kawancen da cewa ba shi da tushe a cikin jama'a, kuma ya dogara ga tallafin kasashen waje (musamman UAE), kuma yana fama da rashin hadin kai da rarrabuwar kawuna.
-
An Kammala Tattakin Yaumul Arba'in 1448h Na Zangon Malumfashi A Najeriya + Hotuna
Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Shaikh Zakzaky (H), masu tattakin Yaumul Arba'in na zangon Malumfashi, sun kammala tattakin, wanda aka fara da safiyar yau Lahadi 18/2/1448 - 2/8/2026.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Taron (International Quds Conference) Karo Na 12 A Abuja Najeriya
Wasu Hotuna na wajen taron (International Quds Conference) Taron ƙasa da ƙasa karo na 12, wanda ya gudana a Abuja, wanda manyan baki suka gabatar da jawabai, daga karshe Jagora Sayyid Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin Rufewa.
-
Shekh Yakub: “Mutum Ba Zai Gane Ƙimar Abin Da Yake A Hannunsa Ba Na Karantarwar Ahlul Baiti (A.S) Sai Ya Zo Karbala”...
Da yammacin yau lahadi (02/08/2026) ne Sheikh Yakub Yahya Katsina ya ziyarci Maukibin Jagoran Harkar Musulunci Sayyid Ibrahim Zakzaky (H), da ke bisa hanyar Tattaki daga Najaf zuwa Karbala, a Amudi na 1117.
-
Iraki: Ta Fara Babban Aiki Na Yaƙi Da Ta'addanci A Nainawa
Iraki a ci gaba da ayyukanta na kawar da sauran ‘yan ta’addan Isil tana ci gaba da sumamen aiki na mussama da bin diddigin ragowar ‘yan ta’addan a lardin Nainawa
-
Shugaban Gabashin Somaliya: "Isra'ila" Tana Burin Babal-Mandab Ne Ba Amincewa Da "Somaliland" Ba
Shugaban jihar arewa maso gabashin Somaliya, Abdul Qadir Ahmed, ya ce amincewar "Isra'ila" ga yankin "Somaliland" yana da alaƙa da muradun tsaro da geopolitical a Bahar Maliya da Babal-Mandab, ba don ba shi cikakken ikon kasa da kasa ga kasar Somaliland ba.
-
Sojojin Najeriya Sun Kubutar Da Mutane 45 Da Aka Yi Garkuwa Da Su
Sojojin Najeriya sun sanar da kubutar da mutane 45 da aka yi garkuwa da su a yayin ayyukan tsaro daban-daban da aka gudanar a jihohin Edo da Borno, tare da kama wasu da ake zargi da haɗin kai da ƙungiyar "ISIS" da kuma wargaza wata ƙungiyar ta’addanci a jihohin Delta da Rivers.
-
Pakistan Ta Yi Watsi Da Rahoton UNAMA Game Da Mutuwar Fararen Hulan Afghanistan
Sojojin Pakistan sun yi watsi da rahoton UNAMA game da mutuwa da raunata fararen hula sama da 1,700 a rikice-rikicen kan iyaka tsakanin Afghanistan da Pakistan, suna kira shi a batu "maras tushe," tare da yin iƙirarin cewa hare-haren ƙasarsu sun kai hari ne kawai ga wuraren ƙungiyoyin da ke ɗauke da makamai.
-
MDD: Hadarin Fataucin Bil'adama A Afghanistan Ya Na Ƙaruwa
Ofishin yaƙi da muggan ƙwayoyi da laifuka na Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadin cewa komawar 'yan gudun hijira sama da miliyan shida, rashin aikin yi, talauci, bin bashin iyalai, da rashin hanyoyin rayuwa na dabam, sun sanya 'yan ƙasar Afghanistan su fuskanci fataucin bil'adama, aikin tilas, da sauran nau'o'in cin zarafi fiye da da.
-
IRGC: Ba Makawa Ga Daukar Fansa Ga Ismail Haniyeh / Makircin Ajiye Makaman Hamas Ya Gaza
Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci na Iran, a ranar tunawa da shahadar jagora Ismail Haniyeh, sun tabbatar da cewa mayar da martani ga wannan ta’addancin tabbatacce ne kuma mai tsanani, sun kuma tabbatar da cewa makircin kwace makaman ƙungiyar Hamas ya ci tura, sun nanata cewa nasara ta ƙarshe ga Falasdinu tana kusa fiye da yadda maƙiya suke zato.
-
Bidiyo | Fifikon Ziyarar Ƙasar Karbala A Kan Ƙasar Ka'aba
Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA –: Imam Sadiq (AS) ya ce mini: Ya zuwa yanzu sau nawa ka yi aikin hajji? Sa na ce: Sau Sha tara. Ya ce: Idan da zaka kai aikin hajji ya kai ga sau ashirin, daidai ya ke (a lada) ga kamar wanda ya ziyarci kabarin Imam Husain (AS) sau ɗaya.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Tarbar Mahalarta Ziyarar Arba'in A Haramin Sayyidah Fatimah Ma’asumah (AS)
An shinfida kabakin Karamci na sayyidah Fatimaa Ma’asumah (AS) a waɗannan kwanakin Arba'in ga mahalarta ziyarar Aba Abdillahil-Husain (AS), kuma babu wani mahalarta da ba zai samu rabonsa daga wannan teburin karamci ba.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Jinjinawa Ga Masu Gudanarwa Na Maukibobin Iraqi A Hanyar Mashaya
Rahoto Cikin Hotuna | Na Jinjinawar Shugaban Maukibin Haramin Sayyidah Fatimah As Ga Masu Gudanarwa Na Maukibobin Iraqi A Hanyar Mashaya
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Taron Al'ada Na "Birnin Muharram" A Dandalin Azadi Tehran
Taron al'ada na hudu na "Brinin Muharram" ya fara gudana tun da yammacin ranar Asabar (1 ga Ogusta 2026) a dandalin Azadi na Tehran, kuma zai ci gaba har zuwa 3 ga Agusta, kowane dare tare da gabatar da shirye-shiryen al'adu, da fasaha, halartar ƙungiyoyin addini, mawkibobin jama'a, da shirye-shiryen Ashura na musamman, yana karɓar bakuncin masu makoki na Aba Abdillahil-Husain (AS) da 'yan ƙasa.
-
Labarai Cikin Hotuna | Na Ci Gaba Da Tattakin Arba’een A Rana Ta Uku Na Yankin Kaduna Najeriya
A rana ta uku an cigaba da gudanar da tattaki a wasu yankuna na jihar Kaduna da suka haɗa da; Tudun Wada, Birnin Gwari, Gadan Gayan, Maraban Jos, Malam Mudi da sauransu.
-
Baqa'i: Duk Wanda Ke Magana Game Da Sakon Annabci, To Ya Auna Yanayin Gwamnatinsa Da Ma'aunin
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqa'i, ya sake tunatar da cewa ƙasarsa ta tabbatu kan manufar kyakkyawar makwabtaka da dangantakar 'yan'uwa tsakanin ƙasashen Musulunci.
-
Jihad Da Hamas: Sun Gana A Alkahira Domin Haɓaka Haɗin Kai Da Kare Al'ummar Falasdinu
Tawagar jagorancin ƙungiyar Hamas karkashin jagorancin shugaban ƙungiyar a Yammacin Kogin Jordan, Zaher Jabarin, ta gana da jagorancin ƙungiyar "Jihadil Islami" karkashin jagorancin babban sakataren ƙungiyar, Ziyad Nakhalah, a babban birnin Masar, Alkahira.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Tariqil-Husain; Hanyar Soyayyar Mahalarta Ziyarar Arba'in Zuwa Karbala Mai Girma
Yayin da ranar Arba'in din Imam Husaini As ake gabatowa, ɗimbin mahalarta ziyara ta hanyar "Tariqul-Husain" a Iraki suna tafiya da ƙafa zuwa Karbala Mai Girma; hanyar da ke da alamu na haɗin kai, hidimar maukibobii, da shaukin Husaini, kowace shekara tana karɓar bakuncin masoya Aba Abdillahil-Husain (AS).
-
Janar Na Amurka: Ba Mu Da Isasshen Ƙarfi Don Kare Isra'ila!
Janar "Alexus Grinkevich," shugaban kwamandancin Amurka a Turai, a cikin wani gargadi da ya rubuta wa ma'aikatar tsaro (Pentagon), ya bayyana cewa saboda matsanancin ƙarancin jiragen ruwan yaƙi (destroyers) da ma'ajiyar tsaro, sojojin ruwa na Amurka ba su da ikon kare ƙasar Amurka da Isra'ila a lokaci guda daga hare-haren makamai masu linzami na Iran da Yemen, kuma Washington a zahiri tana cikin wani mawuyacin hali na dabarar yaki.
-
Rahoto Cikin Bidiyo Da Hotuna | Bayan Sabbin Hare-Haren Isra'ila A Gaza
Hukumomin lafiya na gida sun bayyana cewa hare-hare masu tsanani na Isra’ila a yammacin ranar Juma'a da ranar Asabar a yankunan tsakiya da arewacin zirin Gaza, sun yi sanadin shahadar wasu mutane da dama da kuma raunata wasu da dama.
-
Ayatullah Ramezani A Maukibin Mutanen Afirka, A Tattakin Arba'in:
Daga Makarantar Bilalul-Habashi Zuwa Makarantar Farkawa Ta Imam Shahid; Dangantakar Tarihi Tsakanin Mutanen Afirka Da Ashura
Babban Sakataren Majalisar Duniya ta Ahlul-Bayt (AS), tare da halartar shi a tanti mai lamba 375 ta Tattakin Arba’in, Maukibin mutanen Afirka, ya bayyana wannan nahiya a matsayin babbar dama don fadada farkawar Musulunci, kuma ya ce ƙasashen yamma ta hanyar samar da fuska maras kyau da tsoratarwa game da wannan nahiya, sun samar da damar wawashe albarkatun ƙasa da duwatsu masu daraja.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Na Tattakin Yaumul Arba'een – Rana Ta Uku A Kano Najeriya
Alhamdulillah, a ci gaba da tattakin Yaumul Arba'een na bana a yankin Kano da kewaye, wanda yan uwa musulmai Almajiran sheikh ibraheem zakzaky sukeyi a yau an yada zango a garin Kasuwar dogo, ƙaramar hukumar Bebeji, inda aka gudanar da hutun ɗan lokaci tare da sallah da kuma cin abinci ga mahalarta tattakin.
-
Khatamul-Anbiya: Amurka Tana Tsunduma Cikin Yaƙi Gabaɗaya Na Yanki Ya Kamata Kasashen Yanki Su Sake Nazarin Haɗin Gwiwarsu Da Ita
Kwamandan cibiyar hedikwatar Khatamal-Anbiya (S.A.W, Laftanar Janar Abdul Rahim Abdullahi, ya ce Amurka tana tafiya cikin sauri don tayar da yaƙi gabaɗaya na yanki, yana mai ɗauka cewa wannan hanya tana cikin dabarar da ke da nufin faɗaɗa tasirinta da tilasta mamayarta a yankin.
-
IRGC: Sun Lalata Rumfunan Jirage Mara Matuki Guda Biyu Da Tankin Man Fetur A Sansanin Amurka A Kuwait
Dakarun Juyin Musulunci sun tabbatar da cewa, harin ya haifar da lalata rumfunan jirage mara matuki guda biyu, da tankin man fetur na jiragen sama da jirage masu saukar ungulu na soji a cikin sansanin.
-
-
Iran: Mun Shirya Babban Shiri Don Mayar Da Martani Ga Duk Wata Wautar Amurka Mai Yiwuwa
Mun Shirya Babban Tsari Don Mayar Da Martani Ga Duk Wata Wauta Ta Amurka Mai Yiwuwa
-
Rahoto Cikin Hotuna | Ma'aikatar Cikin Gida Ta Iraki Tana Yin Hidima Ga Maziyartan Arba'in A Karbala Mai Tsarki
Ko da yake wani sashe ne na ma'aikatar cikin gida, wanda ke da ayyuka da wajibai da yawa a duk shekara, amma yana da tasiri a bayyane mai girma a ziyarar Arba'in, inda suke kafa maukibi na masu hidima da yawa, mafi muhimmanci su ne agajin gaggawa na farko, sassan gaggawa, da gungun dakarun likitancin ga jama'a, kuma masu sa kai daga matasa maza da mata suna aiki da ƙwazo, kuma da ƙwarewa mai yawa da suka samu daga horo a cibiyoyin lafiya, da ayyukansu da suka shafe shekaru, su na magani don rage wahalar maziyarta daga gajiya, kasala, da raunuka, da wasu raunukan gaggawa, kafin maganinsu da ayyukansu na likita su zama magani. A kan su akwai gungun hafsoshi ƙwararru, da suke jagorantar wani sashe na soji don cimma manyan manufofi. Duk waɗannan ayyuka a cikin ayukan "Abokan Ma'aikatar Cikin Gida," waɗanda aka rarraba sassansu a Karbala mai tsarki da larduna da dama.
-
Rahoto Cikin Hotuna | Hidimtawar Al’umma Daban-Daban Ga Masu Tattakin Arba'in
Waɗannan fuskoki, musamman masu hidima na ayuka daga larduna daban-daban, da maziyarta masu nufin ziyartar wurin 'yanci na Imam Husain (A.S), ana ganin haƙuri, juriya, haske, da farin cikin samun lada da sakamako a cikinsu; daga cikinsu akwai manya da ƙanana, akwai fari da baƙi, akwai Irakawa, da Larabawa, da sauran baki daga kasashen duniya, duk suna neman samun yardar Allah ta hanyar raya al'amuran Husain (A.S), wanda Imam Sadiq (A.S) ya ce game da su: "Ku raya al'amarinmu, Allah Ya jiƙan wanda ya raya al'amarinmu." Kyamarorin kamfanin dillancin labarai na "Nun" sun ɗauki tarin hotuna na fuskokin masu hidima suna cikin tafiya.