Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa:a yayin taron zagayowar ranar yunkurin mutanen Qom a shekarar 1977, don nuna goyon bayansu ga Imam Khomaini (RA) a kan gwamnatin Pahlavi, dubban mutane daga sassa daban-daban na al’umma a wannan birni, a safiyar yau (Jumma'a) a Husainiyyar Imam Khumaini (RA) sun gana da Jagoran juyin juya halin Musulunci.
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya ce a wani bangare na bayanansa: A daren jiya a Tehran, a wasu wurare, wasu tsirarun masu barna sun zo sun ruguza gini mallakar kasarsu, ta yadda zasu dadada zuciyar shugaban Amurka. Domin ya fadi - wata kalma da ba ta dace ba - cewa idan gwamnatin Iran ta yi abu kaza, zan goyi bayan ku, wannan bangare na wadannan masu tayar da tarzoma da mutane masu cutarwa ga kasar. Suna so da jindadin hakan.
Ya kara da cewa: "Idan shi zai iya tafiyar da kasarsa." Akwai abubuwa daban-daban a kasarsa. Hannunsa yana dauke da jinin Iraniyawa sama da dubu. A yakin kwanaki goma sha biyu mutane sama da dubu daya daga cikin 'yan uwanmu, baya ga kwamandoji, masana kimiyya da dattawa, mutane sun yi shahada.
Ayatullah Khamenei ya ce: Wannan mutum ya ce na bayar da umurni, na jagoranci yakin, don haka ya yarda cewa hannunsa ya gauraya da jinin Iraniyawa, sannan alokacin kuma ya ce ni mai goyon bayan al’ummar Iran ne. Kadan daga cikin mutanen da ba su da kwarewa, marasa hankali da rashin tunani suma sais u yarda kuma su amince har suna aiki bisa ga cimma nufinsa. Sun kunna wuta a cikin shara don su faranta masa.
Ya ci gaba da cewa: "Ya kamata Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran ya ce: Kowa ya san cewa Jamhuriyar Musulunci ta kafu ne da jinin dubban daruruwan mutane don haka wajen maganin masu tada zaune tsaye ba zatai kasa agwiwa ba. Ba zata jure wa 'yan amshin shatan kasashen waje’ Ku koma me kuke so ku zamo ko ‘yan amshin shatan baki kuna aiki don baƙi, to kusani al'umma ta ƙi ku, tsarin Musulunci ya ƙi ku.
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya ce: Wannan Uban da ke zaune a wurin da girman kai yana hukunta duniya baki daya kuma ya san cewa yawanci azzalumai da masu girman kai na duniya kamar Fir'auna da Nimrod da Reza Khan da Mohammad Reza da makamantansu an kifar da su a lokacin da suke sun kasance a kurewar girman kai, haka lamarin yake. Shima wannan za a hambarar da shi.
Ya ci gaba da cewa: Ya ku matasa, ku kiyaye addininku, tunaninku na siyasa, kasancewar ku, shirye-shiryenku, da muhimmancin ku a ci gaban kasa, ku kiyaye hadin kan ku. Ku kiyaye hadin kanku. Al’ummar da take a dunkule tana yin nasara akan dukkan makiyi.
Ra'ayinka