Kamfanin Dillancin Labarai Na AhlulBaiti
26 Maris 2024
Jagora: A Ganawarsa Da Isma'il Haniya "Bamayin Ƙasa A Gwiwa Wajen Goyon Bayan Mutanen Gaza".
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya jaddada cewa kisan gillar da ake yi wa al'ummar Gaza da kuma kisan gillar da ake yi a wannan yanki yana shafar duk wani mai hankali, sannan ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen ba da goyon baya ga al'ummar Palastinu da kuma al'ummar masu da ake zalunta da masu gwagwarmaya a Gaza.
26 Maris 2024
Kwanaki 150 Na Gwabza Yaki: Yadda Isra'ila Ke Tafka Laifukan Yaqi A Gazza.
Wannan makala tana dauke da bayani dangane da irin laifukan yaki da Isra'ila ta tafka a zirin Gazza da kuma kisan kan mai uwa da wabi da ya hada harda 'yan jarida na kasa da kasa, sannan ta kawo jerin sunayen Shahidai na 'yan jarida tun daga farawar yakin har zuwa kwan 150 na yakin.
26 Maris 2024
Adadin Shahidai A Gaza Ya Kai 32,333 Bayan Shahadar Wasu Falasdinawa 107 Wadanda Suka Jikkata Ya Kai 74,694
Adadin shahidan yaki a Gaza ya kai 32,333 sannan adadin wadanda suka jikkata ya kai 74,694 tun daga ranar 7 ga watan Oktoba.
26 Maris 2024
Akwai Bama-Bamai 3,000 Na Yahudawan Sahyuniya Da Ba A Tayar Da Su Ba A Gaza
Rohotanni sun nuna cewa akwai sauran bama-bamai 3,000 da ba’a kaiga tashin su ba inda Yahudawan Sahyuniya ke yin barazana da su ga rayuwar al'ummar Gaza da aka yi wa kawanya.
26 Maris 2024
Rahoto Cikin Hotuna Na Ganawar Da Mawaka Suka Yi Da Jagoran Juyin Juya Hali Musulunci
Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul-Baiti (A.S) – ABNA – ya habarta cewa, a daren haihuwar Karimu Ahlulbaiti, Imam Hasan Mujtabi, gungu na tawagar mawaka da ma'abota al'adu da adabi, sun gana da jagoran juyin juya halin Musulunci Imam Sayyid Ayatullah Ali Khamenei Dz.
26 Maris 2024
Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya Ya Zartas Da Wani Ƙudurin Neman Tsagaita Wuta Cikin Gaggawa A Gaza
Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya zartas da wani kudiri na neman tsagaita wuta cikin gaggawa a Gaza domin watan Ramadan tare da sako mutanen da aka yi garkuwa da su.
25 Maris 2024
Taya Murna Da Zagayowar Ranar Haihuwar Imam Hasan As Shekara Ta Uku Bayan Hijira
Falaloli da darajojinsa sun zo cikin litattafan Shi’a da Ahlus-sunna, kuma ya kasance ɗaya daga As’habul Kisa (Ma’abota bargo) waɗanda ayar taɗhir ta sauka game da su da ƴan shi’a suke imani da ma’asumancinsu, ayar Iɗ’am, ayar mawadda, da ayar mubahala suna daga cikin ayoyin da sauka game da su, Sau biyu yana kyautar bakiɗayan dukiyarsa akan tafarkin Allah, sannan sau uku yana bada kyautar rabin dukiyarsa ga mabuƙata...
23 Maris 2024
Manzon Allah (S.A.W) Ya Ce: “Mafificin Aiki A Cikin Watan Ramadan Shi Ne Nisantar Aikata Sabo”.
Manzon Allah (saww) yana cewa: "Akwai yawa daga masu azumi, wadanda kawai basu da wani kasu na lada daga azuminsu sai ta yunwa da kishirwa".
23 Maris 2024
Labarai Cikin Hotuna Na Yadda Aka Gudanar Da Taron Haɗin Kan Musulmi A Ƙasar Saudiyya
Labarin dake biye ya bayyana yadda wata ƙungiya mai suna Rabidhatul Alamil Islami ta shirya taron haɗin kan dukkan ɓangarorin musulmi na duniya a Ƙasar Saudiya.
22 Maris 2024
An Kai Wa Wani Limamin Harami Hari A Birnin Karachi Na Kasar Pakistan
An kai harin ta'addanci ga limamin harami na garin Shah Faisal na Karachi.
22 Maris 2024
Rahoto Cikin Hotuna Na Gudanar Da Zaman Makokin Rasuwar Sayyida Khadija (AS) A Hubbaren Sayyidina Abbas (AS).
Kamfanin dillancin labaran kasa da kasa na Ahlul-Baiti (A.S) – ABNA – ya habarta cewa: an gudanar da zaman makokin rasuwar Sayyida Khadijah (a.s) a farfajiyar hubbaren Abbas (a.s) da ke birnin Karbala, Mu’alla.
22 Maris 2024
Kudurin Son Zuciya Na Amurka Kan Gaza Bai Samu Karbuwa Ba
Kwamitin Tsaro Na Majalisar Dinkin Duniya Na Kada Kuri'a Kan Kudirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
Kwamitin Sulhu ya kada kuri'a kan kudurin da Amurka ta gabatar' amma kudirin bai kaiga gaci ba saboda ya goyi bayan tseratar da gwamnatin Yahudawa daga hukuntawa daga dukka ayyuakn ta'addancin data gudanar a Gaza.
21 Maris 2024
A Cikin Jawabin Da Ya Yi A Lokacin Ganawa Da Bangarori Daban-daban Na Jama'a;
Jagora: Laifukan Da Ake Aikatawa A Gaza Sun Tabbatar Da Ingancin Kafa Fagen Gwagwarmaya Da Kuma Wajabcin Karfafa Shi.
Imam Khamenei ya ce abubuwan da suke faruwa a zirin Gaza sun tabbatar da wane irin zalunci ne ya mamaye tunani da ayyukan kasashen yammacin duniya masu da'awar wayewa da hakkokin bil'adama, baya ga tabbatar da hakki na kafa bangaren gwagwarmaya da ke kokarin tinkarar zaluncin da ake ci gaba da aiwatar da shi daga fuskancin Masu aikata laifuka na sahyoniyawa akan al'ummar Palastinu.
21 Maris 2024
Juyayin Wafatin Ummul Mu'uminina Sayyidah Khadijah As
A Irin Wannan Ranar Ne dai Sayyadah Khadijah As Tayi Wafati A Shekara Ta Goma Bayan Aiko Manzon Allah Sawa.
20 Maris 2024
Hujjojin Ilimi Kan Tasirin Karatun Kur'ani Da Haddarsa Wajen Inganta Lafiyar Jiki Da Kwakwalwar Musulmi.
Lalle ne Musulmin da suka haddace Al-Qur'ani suna da ingancin rayuwa da rashin damuwa da fargaba.
18 Maris 2024
Ministan Yahudawan Sahyoniya Ya Bukaci A Kashe Haniyah A Qatar
Ministan kudi na gwamnatin sahyoniyawan ya yi kira da a kashe Ismail Haniyah, shugaban ofishin siyasa na kungiyar Hamas a Qatar.
18 Maris 2024
Rundunar Sojan Yaman Sun Gudanar Da Atisayen Tunkarar Yiwuwar Kai Hari Ta Kasa Daga Bangaren Kawancen Amurka
Sassan Cibiyar rundunar sojan Yaman sun gudanar da atisayen tunkarar yiwuwar kai hari ta kasa daga bangaren kawancen Amurka.
17 Maris 2024
Martanin Netanyahu Kan Sukar Amurka:
Netanyahu: Ta Yaya Kuka Manta Da Ranar 7 Ga Oktoba? /Maimakon Ku Matsa Mana Lamba Ku Matsa Iran da Hamas Mana.
Netanyahu ya ce ba zai yi kasa a gwiwa ko mika wuya wajen matsin lamba da Amurka ke yi na dakatar da yakin Gaza, domin a halin da ake ciki, dakatar da yakin na nufin nasarar Hamas.
17 Maris 2024
Nijar Ta Yanke Duk Wata Alakar Yarjejeniyar Soji Da Amurka + Bidiyo
Gwamnatin mulkin sojan Jamhuriyar Nijar ta sanar a daren ranar Asabar da ta gabata cewa ta dakatar da duk wasu yarjejeniyoyin soja da hadin gwiwa da ma'aikatar tsaron Amurka ta Pentagon, wanda hakan ya kawo karshen zaman sojojin Amurka a wannan kasa da ke yammacin Afirka
17 Maris 2024
Ministan Al'adu Da Jagorancin Musulunci A Cikin Sakon Da Ya Aikewa Taron Dangantakar Al'adu Tsakanin Iran Da Venezuela:
Rufe Shafukan Yanar Gizo Na Imam Khamenei Da Meta Ya Yi, Hujja Ce Ta Karyar Da'awar 'Yancin Fadin Albarkacin Baki Na Kasashen Yamma.
A wajen taron "dangantakar al'adu tsakanin Iran da Venezuela" wanda aka gudanar a jami'ar Bolivar ta kasar Venezuela wanda ya samu halartar gungun masana da malaman jami'a, an yi Allah wadai da matakin da Meta ya dauka na cire shafukan da ke goyon bayan Falasdinawa na Imam Khamenei a Instagram da Facebook.